SiyasaAfirka
Yarjejeniyar kawo karshen rikicin Kwango
May 6, 2025Talla
Ministan harkokin wajen kasar Ruwanda, Olivier Nduhungirehe ya tabbatar da cewa za a saka hannu kan yarjejeniyar kawo karshen rikicin da ke faruwa a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango a tsakiyar watan Yuni mai zuwa a birnin Washington na kasar Amurka.
Karin Bayani: Rikicin Kwango na ci gaba da daukar hankalin Jaridun Jamus
Kwararru na Majalisar Dinkin Duniya sun tabbatar da cewa kasar Ruwanda tana goyon bayan 'yan tawayen M23 na gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango da suka kwace wasu yankunan kasar.