SiyasaJamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango
Kwango: SADC za ta janye sojojinta
March 13, 2025Talla
Sojojinta Kungiyar Kasashen Ci-gaban Al'ummar Kudancin Afirka SADC masu yawa ne suka halaka, a watan Janairun wannan shekara ta 2025 da muke ciki. Kungiyar ta SDAC da ke da mambobin kasashe 16 ta bayyana hakan ne yayin wani taro da suka gudanar ta kafar Internet, domin tattauna rikicin yankin da kungiyar 'yan tawayen M23 ta addaba da lakume rayukan miliyoyin mutane na tsawon shekaru 30 tare. Sanarwar bayan taron nasu ta bayyana cewa, ta bayar da umurnin fara janye sojojin rundunar hadakar kasashen ta SAMIDRC daga Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango sannu a hankali.