Rikice-rikiceTurkiyya
PKK ta sanar da shirin ajiye makamanta
May 12, 2025Talla
Sanarwar kungiyar ya zo ne bayan shekaru 40 da ta shafe ta na gwagwarmaya da makami da gwamnatin Turkiyya kan yanci kabilar Kurdawa a kasar.
Taron kungiyar na baya bayan nan ya bijiro da batun sulhunta rikicin Kurdawan ta hanyar dimukuradiyya wanda kungiyar ta ce ta cimma burinta.
Bayan kammala taron a makon da ya gabata, alamu sun nuna kungiyar ta amsa kiran Jagoran da ya kafa kungiyar ta PKK Abdullah Ocalan na su ajiye makamansu.
Ocalan na tsare a gidan yari a wani tsibiri kusa da birnin Santanbul.