Me ya sa 'yan sanda suka mamaye ofishin PDP?
June 30, 2025Talla
‘Yan sanda sun mamaye hedikwatar jam'iyyar adawa ta PDP da ke Abuja, inda suka hana duk jami'ai da ma ‘yayan jamiyyar da suka so gudanar da taron majalisar zartaswar jamiyyar.
Jam'iyyar ta PDP ta dage kan gudanar da taron duk da matakin da hukumar zabe ta dauka na cewa, ba zata hallata jam'iyyar ba domin takaddamar da ke faruwa a kan mukamin sakataren jam'iyyar.
Da kyar daya daga cikin 'yan majalisar zartaswa Chief Bode George ya samu kutsa kaia cikin hedikwatar jam'iyyar.