Yajin aikin ma'aikatan lantarki a Najeriya
August 17, 2022Talla
Kungiyar ma’aikatan tana yajin aikin ne kan wasu korafe-korafe da suka hada da batun karin girma na kanana da manyan ma’aikata da kuma wasu ma’aikatansu da aka sallama daga aiki.
Muazu Ibrahim sakataren kungiyar ma’aikatan wutar lantarkin ya shaida wa wakilinmu da ke Abuja Uwaisu Abubakar Idris cewa ma’aikatan wutar lantarkin sun kashe dukkanin na'urorin wutar lantarki a sassan kasar.